Mutum uku sun mutu, biyar sunji ciwo yayin wani rikici a Bauchi.
Rohoto na cewa mutum uku sun mutu, biyar sun sami rauni a sakamakon arangama tsakanin matasan musulmi da na kirista a Bauchi bayan wani dab dala na bikin tsakiyar dare.
Hakan na zuwa ne bayan wani harin ramukon gayya da matasan musulmi daga Lushi suka kai cikin dare wa yankin ungwan kirista yan tsakani dake cikin garin Bauchi.
An gano cewa matasan musulmin sun shiga gidaje tare kona su da motoci kurmus da kuma afkawa marasa karfi ta hanyar yin anfani da muggan makamai kuma suna yiwa Kansu kirarin yaki.
Lamarin da ya haifar da rundani yayinda Mara sa makamai suka arce don tsira.
An gano cewa rigimar ta fara ne a lokacin da matasan kirista da musulmi suka misayar miyau kafin daga bisani matasan musulmi suka kawo ramukon gayya.
Sai dai kuma harkokin tattalin arziki da zirga zirgan sufuri sun durkushe kuma an tura jami’an tsaro zuwa yankin don kwantar da tarzomar.
Amma Wasu mazauna yankin sun yi bore yayinda yan sanda suka kama Wasu matasan kirista Wanda saura kiris rikici ya barke tsakanin matasan da jami’an tsaro.
Komishinar yan sanda na jihar Bauchi Sunusi Lemu ya tabbatar da kashe mutum uku amma bai ba da adadin wadanda suka sami rauni ba.
Yace rundunar sa ta sami labarin yadda masu kaiwa harin suke kona gidaje da motoci shiya sa ta tura yan sanda don shawo kan lamarin.
More Stories
US RAPPER TORY LANEZ ATTACKED IN PRISON – OFFICIAL
By Oduola F.A. Rapper Tory Lanez, who was convicted over the 2020 shooting of Megan Thee Stallion, was hospitalized after...
HOTJIST FELICITATES WITH HON. TAOHEED ADEBAYO ON APC PRIMARIES VICTORY
By: Sefiu Ajape HOTJIST has congratulated Hon. Taoheed Adebayo Taiwo, popularly known as TAT, on his emergence as the All...
2025 AMVCA: FEMI ADEBAYO, CHIOMA CHUKWUKA WIN BEST ACTOR, ACTRESS AS ‘LISABI’ STEALS THE SPOTLIGHT [FULL LIST]
By Oduola F.A. The 11th Africa Magic Viewers’ Choice Awards (AMVCA) was held at the Eko Hotel and Suites in...
TIMOTHY OMOTOSHO: SOUTH AFRICAN POLICE REARREST NIGERIAN PASTOR CLEARED OF RAPE CHARGES
By: Motunrayo Aniwura South African police rearrested well-known Nigerian televangelist Timothy Omotosho on Saturday, just weeks after his acquittal on...
DHQ REVEALS THOSE BEHIND ATTACKS ON NIGERIAN COMMUNITIES
Agency Report The Defence Headquarters has identified foreign herders as those responsible for the recent violent attacks on local communities...
KANU ADVOCATED FOR BIAFRA ESTABLISHMENT BY ANY MEANS, INCLUDING WAR – WITNESS
By Oduola F.A. The second prosecution witness, identified by the code name BBB, resumed his testimony on Thursday at the...