Mutum uku sun mutu, biyar sunji ciwo yayin wani rikici a Bauchi.
Rohoto na cewa mutum uku sun mutu, biyar sun sami rauni a sakamakon arangama tsakanin matasan musulmi da na kirista a Bauchi bayan wani dab dala na bikin tsakiyar dare.
Hakan na zuwa ne bayan wani harin ramukon gayya da matasan musulmi daga Lushi suka kai cikin dare wa yankin ungwan kirista yan tsakani dake cikin garin Bauchi.
An gano cewa matasan musulmin sun shiga gidaje tare kona su da motoci kurmus da kuma afkawa marasa karfi ta hanyar yin anfani da muggan makamai kuma suna yiwa Kansu kirarin yaki.
Lamarin da ya haifar da rundani yayinda Mara sa makamai suka arce don tsira.
An gano cewa rigimar ta fara ne a lokacin da matasan kirista da musulmi suka misayar miyau kafin daga bisani matasan musulmi suka kawo ramukon gayya.
Sai dai kuma harkokin tattalin arziki da zirga zirgan sufuri sun durkushe kuma an tura jami’an tsaro zuwa yankin don kwantar da tarzomar.
Amma Wasu mazauna yankin sun yi bore yayinda yan sanda suka kama Wasu matasan kirista Wanda saura kiris rikici ya barke tsakanin matasan da jami’an tsaro.
Komishinar yan sanda na jihar Bauchi Sunusi Lemu ya tabbatar da kashe mutum uku amma bai ba da adadin wadanda suka sami rauni ba.
Yace rundunar sa ta sami labarin yadda masu kaiwa harin suke kona gidaje da motoci shiya sa ta tura yan sanda don shawo kan lamarin.
More Stories
POLITICS : RIVERS ASSEMBLY EXTENDS DEADLINE FOR ELECTORAL COMMISSION
The Rivers State House of Assembly has extended the deadline for the summons of the Chairman of the Rivers State...
SUSPECTED LAKUWARA TERRORIST KILLED IN KEBBI BY SECURITY OPERATIVES
A combined team of security operatives, including vigilantes, has killed a suspected Lakurawa terrorist, Maigemu, in Kebbi State. The Director...
LET US TAKE ACTION AGAINST LASSA FEVER- ECOWAS
The Economic Community of West African States, through its specialized health institution, the West African Health Organization has urged researchers,...
UPDATED: SENATE SUSPENDS NATASHA AKPOTI-UDUAGHAN FOR SIX MONTHS
The Senate has suspended Senator Natasha Akpoti-Uduaghen for six months for violation of the Red Chambers rules. Her suspension followed...
SENATOR NATASHA RESUBMITS PETITION AGAINST SENATE PRESIDENT AKAPABIO
Senator Natasha Akpoti-Uduaghan has once again brought before the Senate a petition alleging sexual harassment from Senate President Godswill Akpabio....
CHIEF OF AIRSTAFF ARRIVES ZAMFARA FOR OPERATIONAL VISIT
The Chief of Air Staff, Air Marshal Hassan Abubakar, has arrived in Gusau, the Zamfara State capital, for a one-day...