Sarki Sunusi ya baiwa Dan wasan Kannywood sarauta

Read Time:37 Second
Masarautar kano ta bayyana shirin ta na nadawa mawakin kannywood Naziru M Ahmed sarautan sarkin wakan sarki Muhammad sunusi na biyu.
Sarkin fadar kano munir sunusi ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar ranar lahadi.
A cikin sanarwan masarautar kano ta jinjinawa mawakin saboda yadda yake kaunar masarautar kano da kuma sarki sunusi tun yana rike da sarautar Dan maje
Ahmed ya Dade yana koda sarki sunusi a wakokin sa wanda daya daga ciki yake fatan ya Zama sarki a lokacin wankar sarautar Dan maje tun yana gwamnar baban bankin Najeriya CBN.
Sanarwan ya kara da cewa mawakin ya yi kokarin ganawa da sarkin fadar kano don su shirya yadda za a saka ranar yi masa nadi a matsayin sarkin mawakan sarki sunusi.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %