Ittila’i A Jos yayinda sojoji rufe da fuska suka kashe wani maigadin Banki.

Read Time:41 Second

An cigaba da zaman dar dar a tsakanin mazauna birnin jos biyo bayan kashe wani maigadin banki da wasu sojoji rufe da fuska sukayi akan titin Ahmadu Bello .
Mazauna yankin sun bukaci Adalci wa Linus Edogwu wanda sojojin suka harbeshi da bindiga a bakin kofar shiga bankin.
Wani shaidan gani da ido yace lamarin ya farune a ranar litinin 22 ga watan Oktoba da misalin karfe uku bayan bankin ya daina aiki da kostomomin sa.
Kakakin jami’an soji na musamman karkashin operation safe haven Majo Umar Adams a wata sanarwa daya fitar ya tabbatar da kisan wanda ya bayyana a matsayin abun nadama.
Komandar OPSH yayi amfani da damar wajen gabatarda ta’aziya ga iyalen Edogwu , hukumar gudanarwan bankin da kuma iyalen jami’ai da suka ji ciwo.
Ya jaddada cewa abunda sojojin sukayi ya sabawa ka’idojin aiki.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %