Gwamnatin jihar Benuwe na Neman ayiwa yar shekara goma sha uku Elizabeth Ochanya Adalci.

Read Time:39 Second

mai rike da mukamin Gwamnar jihar Benuwe Benson Abuonu yana nemar ayi Adalci wa Elizabeth Ochanya Ogbaje yar aikin gida da aka yiwa fiyade har ta mutu.
Abuonu wanda ya fitar da sanarwa ta hannun jami’in watsa labarai Mr Ede ogaba Ede ya bayyana lamarin a matsayin rashin imani kuma abun kunya wanda ke bukatar lallai a hukumta wadanda suka aika ta.
Ana zargin cewa Wani baban malami a makarantar kimiya da fasaha ta jihar Benuwe Mr Andrew Ogbuja da Dan sa ne suka yi wa marigayiyar Ochanya fiyade na sawon shekara uku data ke zama da su a matsayin yar aiki.
Gwamnan ya bada tabbacin cewa zasu marawa hukumar yan sanda har sai sun kure karar don hukumta masu laifin ya zama darasi ga masu irin wanan halin shaidanu.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %