Wadanda Ambaliyar ruwa ya Shafa a Kano sun koka da cewa haryanzu ko kobo basu samu ba daga cikin Naira miliyan 100 kudin agaji.

Read Time:34 Second

Wadanda tsira a bala’in Ambaliyan ruwa na kwanan baya a karamar hukumar Rimin Gado na jihar Kano sun ce basu karbi ko sisi ba daga cikin Naira miliyan 100 daya kamata a biyasu biyo bayan Ambaliyan ruwa daya shafi birnin Kano a watan Agusta.
Sun koka da rashin tallafi daga gwamnatin jiha dana tarayya amma a lokacin da aka tuntube shi sekataren hukumar bada agajin gaggawa na jihar Bashir Ali yace hukumar tana kokarin ta taimaka masu.
Shi ma daya ke magana akan lamarin shugaban ayyuka na hukumar NEMA a kano Nura Abdullahi yace hukumar ta sanarda hedkwatar ta a Abuja kuma bada jimawa ba zata fara rarraba kayayyakin agaji ga wadanda abun ya Shafa.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %