Matasa sun kona gidaje a filato saboda sakamakon zabe.

Read Time:39 Second

A ranar Alhamis ne wasu tsagirun matasa suka kona gidaje Hudu a karamar hukumar Langtang da kudu a sakamokon zabe na kananan hukumomi da aka gudanar ranar laraba a jihar filato.
Matasan sun fusata ne a lokacin da Gwamna Simon Bako lalong ya bada sanarwa a gidan Radiyo cewa za a ransar da wadanda suka ci zaben da karfe biyu yayinda su matasan ke jiran baturen zabe ya karbi sakamakonnin zabe da aka gudanar a gundumomi.
Wani shaidar gani da yace gidajen da aka kona mallakar jami’in daya gudanar da zabe a yankin Mr Andrew Sambo da wani fitaccen Dan siyasa a yankin Mr Jackson Ponzhi.
Dayake tabbatar da aukuwar lamarin kakakin yan sandar jihar filato Terna Tyopev yace shima ya samu labarin amma har yanzu bashi da cukakkun bayanai akai.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %