Mutum uku sun mutu, biyar sunji ciwo yayin wani rikici a Bauchi.
Rohoto na cewa mutum uku sun mutu, biyar sun sami rauni a sakamakon arangama tsakanin matasan musulmi da na kirista a Bauchi bayan wani dab dala na bikin tsakiyar dare.
Hakan na zuwa ne bayan wani harin ramukon gayya da matasan musulmi daga Lushi suka kai cikin dare wa yankin ungwan kirista yan tsakani dake cikin garin Bauchi.
An gano cewa matasan musulmin sun shiga gidaje tare kona su da motoci kurmus da kuma afkawa marasa karfi ta hanyar yin anfani da muggan makamai kuma suna yiwa Kansu kirarin yaki.
Lamarin da ya haifar da rundani yayinda Mara sa makamai suka arce don tsira.
An gano cewa rigimar ta fara ne a lokacin da matasan kirista da musulmi suka misayar miyau kafin daga bisani matasan musulmi suka kawo ramukon gayya.
Sai dai kuma harkokin tattalin arziki da zirga zirgan sufuri sun durkushe kuma an tura jami’an tsaro zuwa yankin don kwantar da tarzomar.
Amma Wasu mazauna yankin sun yi bore yayinda yan sanda suka kama Wasu matasan kirista Wanda saura kiris rikici ya barke tsakanin matasan da jami’an tsaro.
Komishinar yan sanda na jihar Bauchi Sunusi Lemu ya tabbatar da kashe mutum uku amma bai ba da adadin wadanda suka sami rauni ba.
Yace rundunar sa ta sami labarin yadda masu kaiwa harin suke kona gidaje da motoci shiya sa ta tura yan sanda don shawo kan lamarin.
More Stories
DON’T QUESTION VARANE’S RETIREMENT DECISION—DESCHAMPS
France coach Didier Deschamps has urged football fans across the world to respect Raphael Varane’s decision to retire from international...
APAPA RECORDS SURGE IN EXPORT VOLUMES, PLANS 2ND EXPORTERS FORUMS
According to APM Terminals Apapa, its half-year (H1'24) non-oil cargo export data were 51,000 Twenty Equivalent Units (TEUs), a rise...
(LIVE UPDATES)#EdoDecides2024: APC WINS OWAN EAST LGA
The Independent National Electoral Commission (INEC) has announced the All Progressives Congress (APC) as the winner of Owan East local...
THIRD MAINLAND BRIDGE VANDAL ARRESTED, OTHERS SOUGHT
Yakubu Yusuf, a suspect, was taken into custody by Lagos Police Command's Onikan Division operators after he vandalized a section...
NATIONAL YOUTH GAMES: TEAM LAGOS INCREASES MEDAL SWEEP
With the state athletes dominating the medals in the 2024 National Youth Games in Delta State, Team Lagos is still...
LAHA, LASHMA HOST CONFERENCE 57 CHAIRMEN ON ILERA EKO
...Champions Pledge To Increase Uptake The Lagos State House of Assembly (LAHA) and the Health Management Agency (LASHMA), in their...