Gwamnatin jihar Kebbi ta dauki sabbin likitoci a aiki.
Read Time:24 Second
Gwamnatin jihar Kebbi ta dauki sabbin likitoci guda Arba’in daga jami’o-in Usman Danfodio , Sakkwato, Sudan da India a aikin gwamnati.
A wata sanarwa daga hannun sekataren watsa labarai na Gwamna Atiku Bagudu , Alhaji Muazu Dakingari ya fitar ranar talata a Kebbi yace an dauki sabbin likitocin ne a aiki kai saye.
Yana mai cewa Gwamnatin jihar ta basu kyautar na’urar laptop guda Arba’in don kara masu kazar kazar.
Yace za a rinka horar da wadanda ke aiki akai akai.
