AN CIGABA DA KASHE MUTANE A ZAMFARA YAYINDA YARI YA KAUCHE
Read Time:33 Second
An cigaba da kashe mutane a Jihar Zamfara yayinda jama’a ke gurnanin cewa Gwamna Abdu’aziz yari ya kauche a Jihar na kwanaki.
Samada mutum Arba’in aka kashe a cikin sati biyu a wani sabuwar hare hare da Barayi da barayin shanu suka kai wasu garuruwa a Jihar.
A ranar litinin akayi gaggarumin zanga zanga a karamar hukumar tsafe saboda yadda Barayi ke kashe mutane.
Gwamna yari yaki ya dawo jihar bayan zanga zangar data yi sanadiyar mutuwar mutane da yawa.
Ya mika ragamar shugabanin jihar wa shugaban majalisar dokokin jihar Sunusi Garba Rikiji kafin ya bar jihar inda ya ajiye mataimakin sa Ibrahim Wakkala Muhammad wanda yake jihar a lokacin.
