Yan sanda sun kama wani mutumin da ya hau karfen baban Allon sanarwa (billboard) sun kai shi ayi masa gwajin tabin hankali.

Read Time:40 Second

Rundunar yan sanda na Jihar Adamawa sun bada Karin bayani akan wani mai suna Lawan Faro wanda ya hau kan baban Allon sanarwa mai Nisan mita Arba’in da kasa a yola yana kira ga shugaban kasa Muhammadu Buhari daya sauka daga mukamin sa.
Lawan wanda yan sanda suka kama shi a ranar Alhamis yace bazai sauka ba har sai dantakaran shugaban kasa a jam’iyar PDP Alh Atiku Abubakar ya tabbatar masa cewa zai doke Buhari a zabe na shekara ta 2019.
Wanan mataki nasa aka ce yana da halaka da sananin talauci a kasar.
Kakakin yan sanda na jihar Adamawa Abubakar Othman yace yanzu mutumin ana kan yi masa aune aune na tabin hankali.
Kakakin yan sanda ya kara da cewa an kai Lawan Asibiti don a gano ko yana da tabin hankali.

Happy
Happy
0 %
Sad
Sad
0 %
Excited
Excited
0 %
Sleepy
Sleepy
0 %
Angry
Angry
0 %
Surprise
Surprise
0 %