An kama wani Dan shekara 35 a lokacin daya ke kokarin sayar da kwayan Ido akan naira dubu dari biyu da Hamsin.
Read Time:34 Second
An kama wani Dan shekara 35 Shuaibu Ibrahim Dan kauyen safiyo a karamar hukumar TOTO na jihar Nasarawa Wanda yan sanda na jihar Niger suka kama da kwayan Ido na mutum.
Acewar rohotanni jami’an sun kama wanda ake zargin ne a sakamakon bayanin tsirri da suka samu daga wani bawan Allah ranar Alhamis.
An ce kwayan idon na wani ne da rikicin igbira da Bassa ya bi ta kansu a jihar Nasarawa.
Jami’in Hulda da jama’a na rundunar Yan sanda a jihar Niger Muhammad Abubakar yace jami’an sun kama Dan asalin jihar Nasarawa ranar Alhamis bayan sun sami kwakwaran bayani daga wani bawan Allah.
Yace za a kai mai laifin kotu bayan an kammala bincike
