Gwamnatin Tarayya tace nan bada jimawa ba zata fara shirin kebe guraren kiwon shanu.
Read Time:24 Second
Ministan aikin gona da raya karkara chif Audu Ogbeh yace nan ga kadan Gwamnatin Tarayya zata fara shirin kebe guraren kiwon shanu a fadin kasar nan don dakatar da kashe kashe da Makiyaya keyi.
Ogbeh ya bayyana hakan ranar litinin a wata ziyara daya kai kasuwar wake dake Auta Balefi , jihar Nasarawa inda yan gudun hijira ne ke harka a kasuwar.
Ministan yakara jaddada kudirin gwamnati na Samar da wasu manyan kasuwanni wa manoma don rage hasarar anfanin gona bayan girbi.
