Boko Haram sun kashe mutum biyu a wani hari kusa da Chibok.
Read Time:30 Second
Mayakan Boko Haram sun kashe mutum biyu a wani kauye kusa da garin Chibok , yankin Arewa maso gabas a Najeriya wasu mazauna kauyen da kuma wakilin mayakan suka shaidawa kamfanin AFP ranar talata.
Mayakan wanda ke biyayya ga Abubakar shekau a tsakiyar Daren litinin suka farma garin Mifah kilomita bakwai tsakanin ta Chibok garin da Boko Haram sukayi Garkuwa da sama da yan mata Dari biyu a shekara ta 2014.
An tura sojoji a yankin da aka sace yan matan bayan shekara shida amma haryanzu Boko Haram na kaiwa hari gari gari a yankin Arewa ta gabas a Najeriya.
