Fursunoni guda Talatin da biyar zasu rubuta jarabawar NECO a jos jihar filato.
Read Time:22 Second
Hukumar kula da gidajen yari na jos tace fursunoni talatin da biyar ne zasu rubuta jarabawan NECO na watan Nuwamba da Disambar bana.
DSP Luka Ayedoo jami’in Hulda da jama’a na rundunar hukumar kula da gidajen yari na jihar ya bayyana hakan wa manaima labarai a jos ranar Lahadi.
Yace kudin jarabawar Asusun bada horo na kasa ITF ce ta biya wa fursunonin daga cikin shagulgulanta na cika shekara Arba’in da bakwai.
